Zab 37:28-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Gama Ubangiji yana ƙaunar abin da yake daidai,Ba ya rabuwa da amintattun jama'arsa,Yana kiyaye su koyaushe,Amma za a kori zuriyar mugaye.

29. Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar,Su gāje ta har abada.

30. Kalmomin mutumin kirki suna da hikima,Yana faɗar abin da yake daidai.

31. Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau.

32. Mugu yakan yi fakon mutumin kirki,Yă yi ƙoƙari yă kashe shi,

Zab 37