Zab 37:23-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Ubangiji yakan bi da mutum lafiyaA hanyar da ya kamata yă bi,Yakan ji daɗin halinsa,

24. In ya fāɗi, ba zai yi warwar ba,Gama Ubangiji zai taimake shiYă tashi tsaye.

25. Yanzu dai na tsufa, ni ba yaro ba ne,Amma ban taɓa ganin Ubangiji ya yar da mutumin kirki ba,Ko kuma a ga 'ya'yansa suna barar abinci.

26. A koyaushe yakan bayar a sake,Yana ba da rance ga waɗansu,'Ya'yansa kuwa dalilin albarka ne.

27. Ka rabu da mugunta ka aikata nagarta,Za ka kuwa zauna a ƙasar har abada,

Zab 37