18. Ubangiji yana kula da masu yi masa biyayya,Ƙasar kuwa za ta zama tasu har abada.
19. Ba za su sha wahala a lokacin tsanani ba,Za su sami yalwa a lokacin yunwa.
20. Amma mugaye za su mutu,Magabtan Ubangiji kuwa za su shuɗe kamar furen jeji,Za su ɓace kamar hayaƙi.
21. Mugu yakan ci bashi, yă ƙi biya,Amma mutumin kirki mai alheri ne,Mai bayarwa hannu sake.
22. Waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka,Za su zauna lafiya lau a ƙasar,Amma waɗanda ya la'antaZa a kore su su fita.
23. Ubangiji yakan bi da mutum lafiyaA hanyar da ya kamata yă bi,Yakan ji daɗin halinsa,
24. In ya fāɗi, ba zai yi warwar ba,Gama Ubangiji zai taimake shiYă tashi tsaye.
25. Yanzu dai na tsufa, ni ba yaro ba ne,Amma ban taɓa ganin Ubangiji ya yar da mutumin kirki ba,Ko kuma a ga 'ya'yansa suna barar abinci.
26. A koyaushe yakan bayar a sake,Yana ba da rance ga waɗansu,'Ya'yansa kuwa dalilin albarka ne.
27. Ka rabu da mugunta ka aikata nagarta,Za ka kuwa zauna a ƙasar har abada,
28. Gama Ubangiji yana ƙaunar abin da yake daidai,Ba ya rabuwa da amintattun jama'arsa,Yana kiyaye su koyaushe,Amma za a kori zuriyar mugaye.
29. Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar,Su gāje ta har abada.
30. Kalmomin mutumin kirki suna da hikima,Yana faɗar abin da yake daidai.
31. Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau.
32. Mugu yakan yi fakon mutumin kirki,Yă yi ƙoƙari yă kashe shi,
33. Amma Ubangiji ba zai bar shi a hannun magabtansa ba,Ko kuwa yă bari a kāshe shiSa'ad da ake masa shari'a.
34. Ka sa zuciyarka ga UbangijiKa kiyaye dokokinsa,Shi zai ba ka ƙarfin da za ka mallaki ƙasar,Za ka kuwa ga an kori mugaye.
35. Na ga wani mugu, azzalumi,Ya fi kowa tsayi,Kamar itacen al'ul na Lebanon,