Zab 37:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Kada ka damu saboda mugaye,Kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba.

2. Za su shuɗe kamar busasshiyar ciyawa,Za su mutu kamar yadda tsire-tsire suke bushewa.

3. Ka dogara ga Ubangiji ka aikata nagarta,Ka zauna a ƙasar, ka sami lafiya.

4. Ka nemi farin cikinka a wurin Ubangiji,Zai kuwa biya maka bukatarka.

5. Ka miƙa kanka ga Ubangiji,Ka dogara gare shi, zai kuwa taimake ka.

Zab 37