Zab 31:20-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Ka ɓoye su a wurinka lafiya daga makircin mutane,A inuwa mai lafiya ka ɓoye su daga zargin magabtansu.

21. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!Gama ya nuna mini ƙaunarsa mai ban al'ajabi,Sa'ad da aka kewaye ni, aka fāɗa mini!

22. Na ji tsoro, na zaci ka jefar da ni ne daga gabanka.Amma ka ji kukana sa'ad da na yi kira gare ka neman taimako.

Zab 31