1. Ya Allahna, ya Allahna,Don me ka yashe ni?Na yi kuka mai tsanani, ina neman taimako,Amma har yanzu ba ka zo ba!
2. Da rana na yi kira a gare ka, ya Allahna,Amma ba ka amsa ba.Da dare kuma na yi kira,Duk da haka ban sami hutawa ba.
3. Amma an naɗa ka Mai Tsarki,Wanda Isra'ila suke yabonsa.