Zab 18:15-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Kashiyar teku ta bayyana,Tussan duniya sun bayyana,Sa'ad da ka tsauta wa magabtana, ya Ubangiji,Sa'ad da kuma ka yi musu tsawa da fushi.

16. Ubangiji ya miƙa hannunsa daga samaniya ya ɗauke ni,Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi.

17. Ya cece ni daga magabtana masu ƙarfi,Daga kuma dukan masu ƙina,Gama sun fi ƙarfina!

18. Sa'ad da nake shan wahala suka auka mini,Amma Ubangiji ya kiyaye ni.

Zab 18