Zab 17:4-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Zancen aikin sauran mutane,Na yi biyayya ga umarninkaBan bi hanyar rashin hankali ba.

5. Ina tafiya a kan tafarkinka kullum,Ban kuwa kauce ba.

6. Ina addu'a gare ka, ya Allah,Domin kakan amsa mini,Don haka ka juyo wurina ka kasa kunne ga maganata.

7. Ka bayyana ƙaunarka mai banmamaki,Ya Mai Ceto,Muddin muna kusa da kai mun tsira daga maƙiyanmu.

8. Ka kiyaye ni kamar yadda ake kiyaye idanu,Ka ɓoye ni a inuwar fikafikanka,

9. Daga hare-hare na mugaye.Maƙiyana cike da ƙiyayya sun kewaye ni.

10. Ba su jin tausayi, suna magana da girmankai,

Zab 17