Zab 147:7-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji,Ku yabi Allah da garaya.

8. Ya shimfiɗa gajimare a sararin al'arshi.Ya tanada wa duniya ruwan sama,Ya sa ciyayi su tsiro a kan tuddai.

9. Yakan ba dabbobi abincinsu,Yakan ciyar da 'ya'yan hankaki sa'ad da suka yi kuka gare shi.

10. Ba ya jin daɗin ƙarfafan dawakai,Ba ya murna da jarumawan mayaƙa.

Zab 147