Zab 135:10-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Ya hallakar da sauran al'umma masu yawa,Ya karkashe sarakuna masu iko, wato

11. Sihon, Sarkin Amoriyawa, da Og, Sarkin Bashan,Da dukan sarakunan Kan'ana.

12. Ya ba da ƙasarsu ga jama'arsa,Ya ba da ita ga Isra'ila.

13. Ya Ubangiji, kullayaumi mutane za su sani kai ne Allah,Dukan tsararraki za su tuna da kai.

14. Ubangiji zai ji juyayin mutanensa,Zai 'yantar da bayinsa.

Zab 135