Zab 130:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A cikin fid da zuciyata,Na yi kira gare ka, ya Ubangiji.

2. Ka ji kukana, ya Ubangiji,Ka kasa kunne ga kiran da nake yi na neman taimako!

3. Idan kana yin lissafin zunubanmu,Wa zai kuɓuta daga hukunci?

4. Amma kakan gafarta mana,Domin mu zama masu tsoronka.

5. Na zaƙu, ina jiran taimako daga Ubangiji,Ga maganarsa na dogara.

6. Ina jiran Ubangiji,Na zaƙu ƙwarai, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir,I, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir.

Zab 130