3. Hakika ya aikata manyan al'amura sabili da mu,Mun kuwa yi farin ciki ƙwarai!
4. Ya Ubangiji, ka komar da mu ƙasarmuKamar yadda ruwan da kake yi yakan koma cikin busassun koguna,
5. Ka sa waɗanda suke kuka a lokacin da suke dashe,Su tattara albarkar kaka da farin ciki!
6. Su waɗanda suka yi kuka a sa'ad da suka fita suna ɗauke da iri,Za su komo ɗauke da albarkar kaka,Suna raira waƙa don farin ciki!