Zab 118:24-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Wace irin rana ce haka da Ubangiji ya ba mu!Bari mu yi farin ciki, mu yi biki!

25. Ka cece mu, ya Ubangiji, ka cece mu!Ka ba mu nasara, ya Ubangiji!

26. Allah yakan sa wa wanda ya zo da sunan Ubangiji albarka!Daga Haikalin Ubangiji muke yabonka!

27. Ubangiji shi ne Allah, yana yi mana alheri,Ku ɗauki hadayunku ku yi ta idi,Ku ɗaura su a zankayen bagade.

Zab 118