Zab 109:25-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. Sa'ad da mutane suka gan ni sun yi mini ba'a,Suna kaɗa kai saboda raini.

26. Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna,Ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka!

27. Ka sa maƙiyana su sani,Kai ne Mai Cetona.

28. Watakila su la'anta ni,Amma kai za ka sa mini albarka,Ka sa a kori waɗanda suke tsananta mini.Da ma ka sa ni da nake bawanka, in yi murna.

Zab 109