23. Saboda wannan Allah ya ce zai hallaka jama'arsa,Amma Musa, zaɓaɓɓen bawansa, ya yi godo ga Allah,Allah kuwa ya huce, bai hallaka su ba.
24. Sai suka ƙi ƙasan nan mai ni'ima,Saboda ba su gaskata alkawarin Allah ba.
25. Suka zauna cikin alfarwansu suna ta gunaguni,Sun ƙi su saurari Ubangiji.
26. Saboda haka ya yi musu kakkausan kashedi,Cewa shi zai sa su duka su mutu a jejin,
27. Zai warwatsa zuriyarsu a cikin arna,Ya bar su su mutu a baƙuwar ƙasa.
28. Sai jama'ar Allah suka taru suka shiga yi wa Ba'al sujada, a Feyor,Suka ci hadayun da aka miƙa wa matattun alloli.
29. Suka tsokani Ubangiji, ya yi fushi saboda ayyukansu,Mugawar cuta ta auka musu,
30. Amma Finehas ya tashi, ya yanke hukunci a kan laifin,Aka kuwa kawar da annobar.
31. Tun daga lokacin nan ake ta tunawa da shi,Saboda abin da ya yi.Za a yi ta tunawa da shi a dukan zamanai masu zuwa.
32. Jama'ar Ubangiji suka sa ya yi fushi.A maɓuɓɓugan Meriba,Musa ya shiga uku saboda su.