Zab 106:13-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Amma nan da nan, suka manta da abin da ya yi,Suka aikata, ba su jira shawararsa ba.

14. Suka cika da sha'awa cikin hamada,Suka jarraba Allah,

15. Sai ya ba su abin da suka roƙa,Amma ya aukar musu da muguwar cuta.

16. Can cikin hamada suka ji kishin MusaDa Haruna, bayin Ubangiji, tsarkaka,

17. Sai ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan,Ta binne Abiram da iyalinsa.

18. Wuta ta sauko bisa magoya bayansu,Ta ƙone mugayen mutanen nan.

19. Suka ƙera ɗan maraƙi da zinariya a Horeb,Suka yi masa sujada.

20. Suka musaya ɗaukakar AllahDa siffar dabba mai cin ciyawa.

21. Suka manta da Allah wanda ya cece su,Ta wurin manyan ayyuka da ya yi a Masar.

22. Kai, Allah ya aikata abubuwa masu ban al'ajabi a can!Ga kuma abubuwa masu banmamaki da ya aikata a Bahar Maliya!

23. Saboda wannan Allah ya ce zai hallaka jama'arsa,Amma Musa, zaɓaɓɓen bawansa, ya yi godo ga Allah,Allah kuwa ya huce, bai hallaka su ba.

24. Sai suka ƙi ƙasan nan mai ni'ima,Saboda ba su gaskata alkawarin Allah ba.

25. Suka zauna cikin alfarwansu suna ta gunaguni,Sun ƙi su saurari Ubangiji.

26. Saboda haka ya yi musu kakkausan kashedi,Cewa shi zai sa su duka su mutu a jejin,

Zab 106