22. Sa'ad da rana ta fito,Sai su koma su kwanta a kogwanninsu.
23. Sa'an nan mutane sukan fita su yi aikinsu,Su yi ta aiki har maraice ya yi.
24. Ya Ubangiji, ka halicci abubuwa masu yawa!Da hikima ƙwarai ka halicce su!Duniya cike take da talikanka.