Yush 4:15-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. “Ko da yake mutanen Isra'ila suna karuwanci,Kada kuma mutanen Yahuza su yi laifi.Kada ku tafi Gilgal,Ko ku haura zuwa Bet-awen.Kada ku yi rantsuwa da cewa,‘Har da zatin Ubangiji!’

16. Mutanen Isra'ila masu taurinkai ne kamar alfadari.Ta yaya Ubangiji zai yi kiwonsuKamar 'ya'yan tumaki a makiyaya mai fāɗi?

17. Mutanen Ifraimu sun haɗa kai da gumaka,Sai a rabu da su.

18. Su taron mashaya ne kawai,Karuwai ne kuma.Suna ƙaunar abin kunya.

19. Iska ta ƙunshe su cikin fikafikanta.Za su ji kunyar bagadansu.”

Yush 4