Yun 4:3-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Domin haka fa, ya Ubangiji, ina roƙonka ka ɗauki raina, gama yanzu gara in mutu da in zauna da rai.”

4. Ubangiji kuwa ya amsa ya ce, “Daidai ne ka yi fushi?”

5. Yunusa ya fita daga birnin, ya yi wajen gabas, ya zauna. Ya yi wa kansa rumfa, ya zauna a inuwarta, yana jira ya ga abin da zai sami birnin.

6. Sai Ubangiji ya sa wata 'yar kuranga ta tsiro ta yi girma a inda Yunusa yake, don ta inuwantar da shi, ya ji daɗi. Yunusa kuwa ya yi murna da wannan 'yar kuranga ƙwarai.

7. Amma kashegari da fitowar rana, sai Allah ya sa tsutsa ta cinye 'yar kurangar har ta mutu.

8. A sa'ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro. Yunusa ya ji kamar zai suma saboda zafin rana da take bugun kansa. Sai ya so ya mutu, ya ce, “Gara in mutu da ina zaune da rai.”

9. Amma Allah ya ce masa, “Daidai ne ka yi fushi saboda 'yar kurangar?”Yunusa ya amsa, “Hakika, daidai ne a gare ni in yi fushi, har ma in yi fushin da ya isa in mutu!”

10. Ubangiji kuma ya amsa, ya ce masa, “Ai, wannan 'yar kurangar dare ɗaya ta girma, kashegari kuma ta mutu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓaci saboda ita!

Yun 4