9. Da ya faɗa musu haka, ya dakata a ƙasar Galili.
10. Bayan 'yan'uwansa sun tafi idin kuwa, shi ma ya tafi, amma a ɓoye, ba a fili ba.
11. Yahudawa suna ta nemansa a wurin idin suna cewa, “Ina yake ne?”
12. Taro kuma suka riƙa maganarsa a raɗe, waɗansu na cewa, “Mutum ne nagari.” Waɗansu kuma na cewa, “A'a, ai, ɓad da jama'a yake.”
13. Amma ba wanda ya yi magana tasa a fili don tsoron Yahudawa.