Yah 7:9-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Da ya faɗa musu haka, ya dakata a ƙasar Galili.

10. Bayan 'yan'uwansa sun tafi idin kuwa, shi ma ya tafi, amma a ɓoye, ba a fili ba.

11. Yahudawa suna ta nemansa a wurin idin suna cewa, “Ina yake ne?”

12. Taro kuma suka riƙa maganarsa a raɗe, waɗansu na cewa, “Mutum ne nagari.” Waɗansu kuma na cewa, “A'a, ai, ɓad da jama'a yake.”

13. Amma ba wanda ya yi magana tasa a fili don tsoron Yahudawa.

Yah 7