Yah 6:6-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Ya faɗi haka ne fa domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.

7. Filibus ya amsa ya ce, “Ai, ko gurasar dinari metan ma ba ta isa ko wannensu ya sami kaɗan ba.”

8. Sai Andarawas ɗan'uwan Bitrus ɗaya daga cikin almajiransa, ya ce masa,

9. “Ga wani ɗan yaro nan da gurasa biyar na sha'ir, da kuma kifi biyu. Amma me waɗannan za su yi wa mutane masu yawa haka?”

10. Yesu ya ce, “Ku ce wa mutane su zauna.” Wuri ne kuwa mai ciyawa. Sai mazaje suka zazzaune, su wajen dubu biyar.

Yah 6