Yah 11:3-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. To, 'yan'uwan nan mata suka aika masa, suka ce, “Ya Ubangiji, ga shi, wanda kake ƙaunan nan ba shi da lafiya.”

4. Da Yesu ya ji haka ya ce, “Wannan rashin lafiya, ƙarshensa ba mutuwa ba ne, domin a ɗaukaka Allah ne, a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurinsa.”

5. Yesu kuwa na ƙaunar Marta da 'yar'uwarta, da kuma Li'azaru.

Yah 11