W. Yah 9:3-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Fāri suka fito zuwa cikin duniya daga cikin hayaƙin nan, aka ba su ikon harbi, irin na kunamin duniya.

4. Aka kuwa hana su cutar ciyayin duniya, ko tsiro, ko kowane itace, sai dai mutanen da ba su da hatimin Allah a goshinsu.

5. Aka kuwa yardar musu su yi musu azaba har wata biyar, amma kada su kashe su, azabarsu kuwa, kamar ta kunama take, in ta harbi mutum.

6. A waɗannan kwanaki kuwa mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba, za su ƙagauta su mutu, mutuwa kuwa sai ta guje musu.

W. Yah 9