25. Sai dai ku riƙi abin da kuke da shi kankan, har in zo.
26. Duk wanda ya ci nasara, yake kuma kiyaye aikina har ƙarshe, shi zan bai wa iko a kan al'ummai,
27. zai kuwa mallake su da sanda ta ƙarfe, ya farfashe su kamar tukwanen yumɓu
28. (kamar yadda Ni ma kaina na sami iko a gun Ubana), zan kuma ba shi gamzaki.
29. Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”