W. Yah 18:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Bayan haka, na ga wani mala'ika yana saukowa daga Sama, mai iko da yawa, sai aka haskaka duniya da ɗaukakarsa.

2. Sai ya yi kira da murya mai ƙarfi, ya ce,“Ta fāɗi! Babila mai girma ta fāɗi!Ta zama mazaunin aljannu,Matattarar kowane baƙin aljani,Da kowane irin ƙazamin tsuntsu, abin ƙyama.

3. Dukkan al'ummai sun yi tsananin jarabar yin fasikanci da ita,Sarakunan duniya kuma sun yi fasikanci da ita,Attajiran duniya kuma sun arzuta da almubazzarancinta.”

4. Sai na ji wata murya daga Sama, tana cewa,“Ku fito daga cikinta, ya ku jama'ata,Kada zunubanta su shafe ku,Kada bala'inta ya taɓa ku.

5. Domin zunubanta sun yi tsororuwa, sun kai har Sama,Allah kuwa ya tuna da laifofinta.

W. Yah 18