W. Yah 1:10-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. A ranar Ubangiji ya zamana Ruhu ya iza ni, sai na ji wata murya mai ƙara a bayana kamar ta ƙaho,

11. tana cewa, “Rubuta abin da ka gani a littafi, ka aika wa ikilisiyoyin nan bakwai, wato ta Afisa, da ta Simirna, da ta Birgamas, da ta Tayatira, da ta Sardisu, da ta Filadalfiya, da kuma ta Lawudikiya.”

12. Sai na juya in ga wanda yake yi mini magana, da juyawata kuwa, sai na ga fitilu bakwai na zinariya.

13. A tsakiyar fitilun nan kuwa, na ga wani kamar Ɗan Mutum, saye da riga har idon sawu, ƙirjinsa kuma da ɗamarar zinariya.

14. Kansa da gashinsa farare fat ne kamar farin ulu, farare fat kamar alli, idanunsa kamar harshen wuta,

W. Yah 1