Neh 6:15-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. A cikin kwana hamsin da biyu aka gama garun, ran ashirin da biyar ga watan Elul.

16. Sa'ad da abokan gābanmu da dukan al'umman da suke kewaye da mu suka ji, sai suka ji tsoro, gabansu kuma ya faɗi, gama sun gane, da taimakon Allahnmu muka yi wannan aiki.

17. A kwanakin nan kuma shugabannin Yahuza suka yi ta aika wa Tobiya da wasiƙu, shi kuma Tobiya yana ta aika musu da nasa wasiƙu.

Neh 6