Mat 9:18-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Yana cikin yi musu magana haka, sai ga wani shugaban jama'a ya zo, ya yi masa sujada, ya ce, “Yanzu yanzu 'yata ta rasu, amma ka zo ka ɗora mata hannu, za ta rayu.”

19. Sai Yesu ya tashi, ya bi shi tare da almajiransa.

20. Ga kuma wata mace wadda ta shekara goma sha biyu tana zub da jini, ta raɓo ta bayansa, ta taɓa gezar mayafinsa,

21. domin ta ce a ranta, “Ko da mayafinsa ma na taɓa, sai in warke.”

Mat 9