8. Kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatarku tun kafin ku roƙe shi.
9. Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka,‘Ya Ubanmu, wanda yake cikin Sama,A kiyaye sunanka da tsarki.
10. Mulkinka yă zo,A aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a Sama.
11. Ka ba mu abincinmu na yau.
12. Ka gafarta mana laifofinmu,Kamar yadda mu ma muke gafarta wa waɗanda suke yi mana laifi.