7. “In kuwa kuna addu'a, kada ku yi ta maimaitawar banza, kamar yadda al'ummai suke yi, a zatonsu za a saurare su saboda yawan maganarsu.
8. Kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatarku tun kafin ku roƙe shi.
9. Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka,‘Ya Ubanmu, wanda yake cikin Sama,A kiyaye sunanka da tsarki.