66. Me kuka gani?” Suka amsa suka ce, “Ya cancanci kisa!”
67. Sai suka tattofa masa yau a fuska, suka bubbuge shi, waɗansu kuma suka mammare shi,
68. suna cewa, “Yi mana annabci, kai Almasihu! Faɗi wanda ya buge ka!”
69. To, Bitrus kuwa yana zaune a tsakar gida a waje, sai wata baranya ta zo ta tsaya a kansa, ta ce, “Kai ma, ai, tare kake da Yesu Bagalile!”
70. Amma ya musa a gabansu duka ya ce, “Ni ban san abin da kike nufi ba.”