46. Albarka tā tabbata ga bawan da in ubangidansa ya dawo zai samu yana yin haka.
47. Hakika, ina gaya muku, sai ya ɗora shi a kan dukan mallakarsa.
48. Amma in bawan nan mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Ubangidana ya jinkirta zuwansa,’
49. sa'an nan ya soma dūkan abokan bautarsa, yana ci yana sha tare da mashaya,
50. ai, ubangidan wannan bawa zai zo a ranar da bai zata ba, a kuma lokacin da bai sani ba,
51. yă farfasa masa jiki da bulala, ya ba shi rabonsa tare da munafukai. Nan za a yi kuka da cizon baki.”