4. Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku kula fa kada kowa ya ɓad da ku,
5. domin mutane da yawa za su zo da sunana, suna cewa, su ne Almasihu, har su ɓad da mutane da yawa.
6. Za ku kuma riƙa jin labarin yaƙe-yaƙe da jitajitarsu. Kada fa hankalinku ya tashi, don lalle ne a yi haka, amma ƙarshen tukuna.
7. Al'umma za ta tasar wa al'umma, mulki ya tasar wa mulki. Za a kuma yi yunwa da raurawar ƙasa a wurare dabam dabam.
8. Amma fa duk wannan masomin azaba ne tukuna.
9. “Sa'an nan za su bashe ku, a ƙuntata muku, su kuma kashe ku. Duk al'ummai za su ƙi ku saboda sunana.
10. A sa'an nan da yawa za su yi tuntuɓe, su ci amanar juna, su kuma ƙi juna.