Mat 13:7-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Waɗansu kuma suka faɗa cikin ƙaya, sai ƙaya ta tashi ta sarƙe su.

8. Waɗansu kuma suka faɗa a ƙasa mai kyau, suka yi tsaba, waɗansu riɓi ɗari ɗari, waɗansu sittin sittin, waɗansu kuma talatin talatin.

9. Duk mai kunnen ji, yă ji.”

10. Sai almajiran suka zo, suka ce masa, “Me ya sa kake musu magana da misalai?”

11. Ya amsa musu ya ce, “Ku kam, an yarda muku ku san asiran Mulkin Sama, amma su ba a ba su ba.

12. Domin mai abu akan ƙara wa, har ya yalwata. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.

Mat 13