14. In kuma za ku karɓa, shi ne Iliya da dā ma zai zo.
15. Duk mai kunnen ji, yă ji.
16. “To, da me zan kwatanta zamanin nan? Kamar yara ne da suke zaune a kasuwa, suna kiran abokan wasansu, suna cewa,
17. ‘Mun busa muku sarewa, ba ku yi rawa ba,Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba!’