2. “Ina jin tausayin wannan taro, don yau kwanansu uku ke nan a guna, ba su da wani abinci.
3. In kuwa na sallame su su tafi gida da yunwa haka, ai, za su kasa a hanya, ga shi kuwa, waɗansunsu sun fito nesa.”
4. Sai almajiransa suka amsa masa suka ce, “Ina za a iya samun gurasar da za ta ciyar da mutanen nan a jeji haka?”