Mar 6:37-40 Littafi Mai Tsarki (HAU)

37. Amma ya amsa musu ya ce, “Ku ku ba su abinci mana.” Sai suka ce masa, “Wato mu je mu sayo gurasa ta dinari metan, mu ba su su ci?”

38. Ya ce musu, “Gurasa nawa gare ku? Ku je ku dubo.” Da suka binciko suka ce, “Ai, biyar ne, da kifi biyu.”

39. Sa'an nan ya yi umarni dukkansu su zazzauna ƙungiya ƙungiya a ɗanyar ciyawa.

40. Haka suka zauna jeri jeri, waɗansu ɗari ɗari, waɗansu hamsin hamsin.

Mar 6