15. Da suka zo wurin Yesu suka ga mai aljannun nan a zaune, saye da tufa, cikin hankalinsa kuma, wato mai aljannun nan masu yawa a dā, sai suka tsorata.
16. Waɗanda aka yi abin a kan idonsu kuwa, suka farfaɗi abin da ya gudana ga mai aljannun da kuma aladen.
17. Sai suka fara roƙon Yesu ya bar musu ƙasarsu.
18. Yana shiga jirgi ke nan, sai mai aljannun nan a dā ya roƙe shi izinin zama a gunsa.