23. Sai Yesu ya kira su, ya ba su misali da cewa, “Ina Shaiɗan zai iya fitar da Shaiɗan?
24. Ai, in mulki ya rabu a kan gāba, wannan mulki ba zai ɗore ba.
25. Haka in gida ya rabu a kan gāba, wannan gida ba zai ɗore ba.
26. Shaiɗan kuma in ya tayar wa kansa, ya rabu, ba zai ɗore ba, ƙarewa tasa ce ta zo.