Mar 15:7-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Akwai wani wai shi Barabbas da yake ɗaure, tare da waɗansu 'yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin tawayen.

8. Jama'a fa suka matso, suka fara roƙon Bilatus ya yi musu abin da ya saba yi.

9. Sai ya amsa musu, ya ce, “Wato kuna so ne in sakar muku Sarkin Yahudawa?”

10. Don ya gane, saboda hassada ne manyan firistoci suka bashe shi.

11. Amma manyan firistocin suka zuga jama'a, gwamma ya sakar musu Barabbas.

12. Sai Bilatus ya sāke ce musu, “To, ƙaƙa zan yi da wanda kuke kira Sarkin Yahudawa?”

13. Sai suka sāke yin ihu suka ce, “A gicciye shi!”

14. Bilatus ya ce musu, “Ta wane hali? Wane mugun abu ne ya yi?” Amma su, sai ƙara ɗaga murya suke yi, suna cewa, “A gicciye shi!”

15. Bilatus kuwa da yake yana son ƙayatar da jama'a, ya sakar musu Barabbas. Bayan ya yi wa Yesu bulala, ya ba da shi a gicciye shi.

Mar 15