25. Hakika, ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabi ba, sai dai a ranan nan da zan sha wani sabo a Mulkin Allah.”
26. Da suka yi waƙar yabon Allah, sai suka fita suka tafi Dutsen Zaitun.
27. Yesu ya ce musu, “Duk za ku yi tuntuɓe ne, domin a rubuce yake cewa, ‘Zan bugi makiyayi, tumaki kuwa su fasu.’
28. Amma fa bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa ƙasar Galili.”