8. Sai suka kama shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge.
9. To, me ubangijin garkan nan zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba waɗansu garkar.
10. Ashe, ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba? cewa,‘Dutsen da magina suka ƙi,Shi ne ya zama mafificin dutsen gini.
11. Wannan aikin Ubangiji ne,A gare mu kuwa abin al'ajabi ne.’ ”