Mar 10:4-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Suka ce, “Musa ya ba da izini a rubuta takardar kisan aure, a kuma saki matar.”

5. Yesu ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya rubuta muku wannan umarni.

6. Amma tun farkon halitta ‘Allah ya halicce su, namiji da tamata.’

7. ‘Don haka fa sai mutum yă bar uwa tasa da ubansa, yă manne wa mata tasa.

8. Haka su biyun nan su zama jiki guda.’ Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne.

9. Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.”

Mar 10