21. Suka shiga Kafarnahum. Ran Asabar kuwa, ya shiga majami'a yana koyarwa.
22. Sun yi mamakin koyarwa tasa, domin yana koya musu da hakikan cewa, ba kamar malaman Attaura ba.
23. Nan take sai ga wani mutum mai baƙin aljan a majami'arsu, yana ihu,
24. yana cewa, “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne ka hallaka mu? Na san ko wane ne kai, Mai Tsarkin nan ne kai na Allah.”
25. Yesu ya kwaɓe shi ya ce, “Yi shiru! Rabu da shi!”