M. Sh 27:13-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Waɗannan za su tsaya a bisa kan Dutsen Ebal don su la'anta, wato kabilar Ra'ubainu, da ta Gad, da ta Ashiru, da ta Zabaluna, da ta Dan, da ta Naftali.

14. Sa'an nan Lawiyawa za su ta da murya, su ce wa dukan Isra'ilawa:

15. “ ‘La'ananne ne mutumin da ya sassaƙa, ko ya ƙera gumaka, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannun mai sana'a, ya kafa ta a ɓoye.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

16. “ ‘La'ananne ne wanda ya raina mahaifinsa ko mahaifiyarsa.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

17. “ ‘La'ananne ne wanda ya ci iyakar maƙwabcinsa.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

18. “ ‘La'ananne ne wanda ya karkatar da makaho daga hanya.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

M. Sh 27