12. sai ku yanke hannunta, kada ku ji tausayi.
13. “Kada ku riƙe ma'aunin nauyi iri biyu a jakarku, wato babba da ƙarami.
14. Kada kuma ku ajiye mudu iri biyu a gidanku, wato babba da ƙarami.
15. Sai ku kasance da ma'aunin nauyi da mudu masu kyau don ku daɗe a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
16. Gama duk wanda yake aikata irin waɗannan abubuwa, da dukan marasa gaskiya, abin ƙyama ne su ga Ubangiji Allahnku.”