M. Sh 25:12-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. sai ku yanke hannunta, kada ku ji tausayi.

13. “Kada ku riƙe ma'aunin nauyi iri biyu a jakarku, wato babba da ƙarami.

14. Kada kuma ku ajiye mudu iri biyu a gidanku, wato babba da ƙarami.

15. Sai ku kasance da ma'aunin nauyi da mudu masu kyau don ku daɗe a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.

16. Gama duk wanda yake aikata irin waɗannan abubuwa, da dukan marasa gaskiya, abin ƙyama ne su ga Ubangiji Allahnku.”

M. Sh 25