12. “Za ku keɓe wani wuri a bayan sansani inda za ku riƙa zagayawa.
13. Sai ku ɗauki abin tona ƙasa tare da makamanku. Lokacin da za ku zagaya garin yin najasa, sai ku tsuguna ku tona rami da abin tona ƙasa sa'an nan ku rufe najasar da kuka yi.
14. Gama Ubangiji Allahnku yakan yi yawo cikin sansaninku don ya cece ku, ya ba da magabtanku cikin hannunku. Saboda haka dole ku tsabtace sansaninku don kada Ubangiji ya iske wata ƙazanta a cikinku, ya rabu da ku.”
15. “Kada ku ba da bawan da ya tsere, ya zo gare ku, ga ubangijinsa.
16. Zai zauna a wurinku. Sai ya zauna tare da ku, a wurin da ya zaɓa cikin garuruwanku inda ya fi so. Kada ku dame shi.
17. “Kada Isra'ilawa mata da maza su shiga ƙungiyar karuwanci na addini.