17. Yana zarginta da aikata abin kunya, ya ce, bai iske 'yarmu budurwa ba. Amma ga shaidar budurcin 'yata.’ Sai su shimfiɗa tsalala a gaban dattawan.
18. Sai dattawan garin su kama mutumin su yi masa bulala,
19. su ci shi tara shekel ɗari na azurfa, su ba mahaifin yarinyar, gama a fili mutumin ya ɓata sunan budurwar cikin Isra'ila. Za ta zama matarsa, ba shi da iko ya sake ta muddin ransa.
20. “Idan aka tabbatar zargin gaskiya ne, ba a kuma ga shaidar budurcinta ba,