4. Idan mai mulki ya husata da kai, kada ka bar inda kake, gama kwantar da hankali yakan sa a yafe manyan laifofi.
5. Akwai mugunta wadda na gani a duniya, wato kuskuren da masu mulki suke yi.
6. Ana ba wawaye manyan matsayi, attajirai kuwa ana ƙasƙantar da su.
7. Na taɓa ganin bayi a kan dawakai, shugabanni kuwa suna tafiya a ƙasa kamar bayi.
8. Wanda ya haƙa rami shi ne zai fāɗa a ciki. Wanda kuma ya rushe katanga, shi maciji zai sara.
9. Wanda yake farfasa duwatsu shi za su yi wa rauni. Wanda kuma yake faskare itace yana cikin hatsarinsu.