Luk 24:43-50 Littafi Mai Tsarki (HAU)

43. Ya kuwa karɓa, ya ci a gabansu.

44. Ya kuma ce musu, “Wannan ita ce maganata da na gaya muku tun muna tare, cewa lalle ne a cika duk abin da yake rubuce game da ni a Attaura ta Musa, da littattafan annabawa, da kuma Zabura.”

45. Sa'an nan ya wayar da hankalinsu su fahimci Littattafai,

46. ya kuma ce musu, “Haka yake a rubuce, cewa wajibi ne Almasihu ya sha wuya, a rana ta uku kuma ya tashi daga matattu,

47. a kuma yi wa dukan al'ummai wa'azi su tuba, a gafarta musu zunubansu saboda sunansa. Za a kuwa fara daga Urushalima.

48. Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.

49. Ga shi, ni zan aiko muku da abin da Ubana ya alkawarta. Amma ku dakata a birni tukuna, har a yi muku baiwar iko daga Sama.”

50. Sai ya kai su waje har jikin Betanya. Ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.

Luk 24